Friday, November 30, 2018

RAKA'A (2) DA SUKAFI DUNIYA DA ABUN DA KE CIKINTA



ﻗﺎﻝ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ: ﺭﻛﻌﺘﺎ ﺍﻟﻔﺠﺮ ﺧﻴﺮ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻧﻴﺎ
ﻭﻣﺎ ﻓﻴﻬﺎ . ‏( ﺭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ )
Manzon Allah (S.A.W) yace: Raka'o'i biyu sun fi
Duniya alkhairi da abun ke cikinta. (Muslim ne ya
rawaito)
Wace Sallace Wannan, Kuma a wana lokaci ake so
mutum yayita?
= Wannan Sallan itace Rakatayil Fajr, me raka'a
biyu, wacce ake yinta bayan futowan Alfijir, kuma
kafin a shiga Sallahn Asuba.
Ya tabbata acikin Hadisi, Manzon Allah (S.A.W) yana
karanta Fatiha ne acikin duk raka'a biyun.
Haka nan a wani Hadisin ma ya tabbatar da
Manzon Allah S.A.W ya karanta (Qul ya ayyul
kafirun a raka'an farko da Qul Huwallahu a raka'a
ta fiyu). Duk wanda mutum ya ɗauka yayi dai-dai.
GA HADISAN DA SUKA TABBATAR DA HAKAN:
1. ﻭﻋﻦ ﻋﺎﺋﺸﺔ — ﺭﺿﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ — ﻗﺎﻟﺖ: ﻛﺎﻥ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ
ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻳﺨﻔﻒ ﺍﻟﺮﻛﻌﺘﻴﻦ ﺍﻟﻠﺘﻴﻦ ﻗﺒﻞ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺼﺒﺢ ﺣﺘﻰ
ﺇﻧﻲ ﺃﻗﻮﻝ : ﺃﻗﺮﺃ ﺑﺄﻡ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ؟ ‏( ﻣﺘﻔﻖ ﻋﻠﻴﻪ )
2. ﻭﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ – ﺭﺿﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ – ﺃﻥ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ
ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺮﺃ ﻓﻰ ﺭﻛﻌﺘﻰ ﺍﻟﻔﺠﺮ: ﻗﻞ ﻳﺎ ﺃﻳﻬﺎ ﺍﻟﻜﺎﻓﺮﻭﻥ، ﻗﻞ ﻫﻮ ﺍﻟﻠﻪ ﺃﺣﺪ .
‏( ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ )
1. An karɓo hadisi daga Aisha Allah ya ƙara mata
yarda tace: Annabin Allah S.A.W ya kasance yana
sauƙaƙe raka'o'i biyu waɗanda suke kafin Sallahn
Asuba har sai nace: Shin kana karanta fatiha ma
kuwa? (Bukhari da Musim suka rawaito)
2. An karɓo Hadisi daga Abu Huraira Allah ya ƙara
masa yarda– Allah Annabi S.A.W ya karanta acikin
Raka'atal Fajr Qul Yaa ayyuhal kafirun, Qul
Huwallahu Ahad. (Muslim ne ya rawaito)
Ɗan uwa, Yar uwa!
Kar abarmu a baya, domin wannan wata dama ce
agaremu baki ɗaya na samun soyayyar Allah da
kuma tsira a duniya da lahira, idan muka dauwama
akan aikin alkhairi irin waɗan nan.
Manzon Allah (S.A.W yace: Mafi soyuwan ayyuka
agurin Allah, sune waɗan da aka dauwama ana
aikatasu ko da kuwa ƴan kaɗan ne.
Yaa Allah, Ka dauwamar da mu akan aikata irin
wanga ayyuka na alkhairi.

No comments:

Post a Comment