Friday, November 30, 2018

MUTANE NAU'I BIYU NE



ﻗﺎﻝ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ: ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺭﺟﻼﻥ: ﻋﺎﻟﻢٌ ﻭﻣﺘﻌﻠﻢٌ،
ﻭﻻ ﺧﻴﺮ ﻓﻰ ﺳﻮﺍﻫﻤﺎ . ‏( ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ )
Manzon Allah (S.A.W) yace: Mutane kala biyu ne:
Me ilimi da me neman ilimi, babu alkhairi ga waɗan
da basu ba. (Ɗabrani ne ya rawaito)
Duk mutumin da be kasance cikin jerin mutane
biyun nan ba, wato me ilimi ko kuma me neman
ilimi, to tabbas ba ze samu wannan alkhairi ba,
hasali ma shi mutacce ne. Kamar yanda Manzon
Allah ya faɗa acikin Hadisi.
Kuma ilimin da ake magana anan shine na addini.
Domin shi kaɗai ne aka wajabta mana nema wala
mace, wala namiji. Saboda da ilimin addini kaɗai
zaka san yanda zaka cika alƙawuran da ka ɗauka
ma Allah tun kana cikin mahaifiyarka cewa: Zaka
bauta ma Allah shi kaɗai, ba zaka haɗa shi da
komai ba wajen bauta. Kuma hakan ba ze yuwu ba
se da ilimi.
Amma ba wai ilim zamani ake nufi ba, wanda shima
yana da nashi amfanin sosai. Amma ka tabbata
kayi ilimin addininka kafin na zamani.
Domin duk duniya babu # jahili se wanda bashi da
ilimin addini ittifaƙan.
Ya Allah, ka bamu ilimin addininKa me amfani.
Aameen...

No comments:

Post a Comment